13/08/2025
13th August, 2004 - 13th August, 2025
A Yau Talata 13th August, 2025 mai girma Sarkin Gadau/Hakimin kasar Gadau yake cika shekaru ashirin da daya (21) chif-chif a matsayin hakimi a masarautar Katagum.
Sarkin Gadau/Hakimin kasar Gadau, Alh Muhammadu Gadau dan Sarkin Gadau Muhammadu Baffah ne, kuma jika ne ga Sarkin Katagum na farko Mallam Ibrahim Zaki.
Gadau ta samu ci gaba sosai a sanadiyyar zuwan mai girma Hakimi, wadanda idan aka ce za a zayyano su, to lokaci ba zai bari bah.
Amman ga kadan daga ciki:
1. Hakimin Gadau, shi ne ya nemo titin da ke cikin Gadau a Saudi-Arebiyya, lokacin yana amirul-hajji, suna zaune daki daya da mai girma Governor Ahmad Adamu Mu'azu, wadda a take governor ya yi masa wannan alfar. Ba su bar Makka bah aka fara aikin titin Gadau.
2. Jejin nomah na Rafin Gabu: Sanin kowa ne a da jeji ne wadda ba wani abu da ake nomawa a cikinsa, Mai girma Hakimin Gadau shi ne mutum na farko daya fara farfafo da noma a jejin rafin Gabu bayan shekaru da yawa, wadda ya fara noman alkama kafin nan aka fara noman shinkafa.
3. Kafin zuwan mai girma Hakimi, Gadau babu network, wadda cikin hukuncin Allah a yanxu ba irin network din da ba mu dashi a Garin Gadau.
4. Haka zalika a fannin ilimi, sarki ya taka rawar gani matukar gaya, wadda a zuwansa ne ya samo manah.
i. Day primary school
ii. Day secondary school
iii. Upper basic secondary school
iv. Uwa uba kuma, jami'ar Jahar Bauchi. Mai Girma hakimi ya taka rawar gani matuka wajen samar da wannan jami'a ta Bauchi dake garin Gadau, tare da taimakawar Santurakin Katagum Santurakin Katagum(Alhaji Sulaiman Sa'adu Lokacin suna tare da Governor) da su Babayo Garba Gamawa (Allah ya masa rahama), wacce Mai girma governor Mal. Isah Yuguda ya bude ta a wannan Gari na Gadau. Amma ba kowa ya San da hakan ba, sai 'yan kadan. Wasu sun kalli Jami'ar ne, amma ba a San TA yaya akai ta zo ba. (Allah ya saka musu da alkhairi