Daular Dan Fodio Jiya Da Yau

Daular Dan Fodio Jiya Da Yau Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Daular Dan Fodio Jiya Da Yau, History Museum, Makwarari, Kano.

Uba Bai fi Uba Ba Kuja Kunnen wadannan Marasa Kunyar Kafin Mutaso
09/06/2026

Uba Bai fi Uba Ba
Kuja Kunnen wadannan Marasa Kunyar Kafin Mutaso

Agobe Lahadi Ne Za'afara Duban Jininirin Watan Zulhijja Bisa umarnin Mai Alfarma Sarkin Musulmin Nigeria
16/05/2026

Agobe Lahadi Ne Za'afara Duban Jininirin Watan Zulhijja Bisa umarnin Mai Alfarma Sarkin Musulmin Nigeria

Kiyayyar Da Sukeyiwa Dan fodiye Ta Samo Asali Ne Tun Daga Kiyayyar Su Ga Addinin Musulunci Da Kuma Ma'aiki Sallallahu Al...
16/05/2026

Kiyayyar Da Sukeyiwa Dan fodiye Ta Samo Asali Ne Tun Daga Kiyayyar Su Ga Addinin Musulunci Da Kuma Ma'aiki Sallallahu Alaihi Wa Sallama
Via: RMB MAKWARARI

"DAULAR DAN FODIYE JIYA DA YAU"Dan Uwa Baka Da Aiki Illa Karanta Littattafan Turawa Sun s**ar Shehu Dan Fodio Suna Aibat...
14/05/2026

"DAULAR DAN FODIYE JIYA DA YAU"
Dan Uwa Baka Da Aiki Illa Karanta Littattafan Turawa Sun s**ar Shehu Dan Fodio Suna Aibata Jihadin Shi Kuma Ka Kasa Karanta Littafi إنفاق الميسور B***e Kasan Gaskiyar Abin Da Ya Faru Daga Bakin SOJAN DAULAR DAN FODIO KWAMANDAN YAQI SHEHU MUHAMMADU BALLO To wallahi Abin Kunya Ne Gare ka Lallai Kayi Kokari Kazo Kasan Abinda Ya Faru Takan Wannan Littafi Mai Albarka Gashi Da Dadin Karantawa Malam

DAULAR DAN FODIO JIYA DA YAUFITOWA TA BIYU:"HAUSAWA DA ASALIN SU, ASALIN KALMAR HAUSA,MAZAUNIN SU, AL'ADUN SU, ILIMIN SU...
13/05/2026

DAULAR DAN FODIO JIYA DA YAU

FITOWA TA BIYU:

"HAUSAWA DA ASALIN SU, ASALIN KALMAR HAUSA,MAZAUNIN SU, AL'ADUN SU, ILIMIN SU.WASANNIN SU, SANA'O'IN SU, ADDININAN SU,"

ASALIN HAUSAWA:

HAUSAWA: wani jinsi ne na jama'a da s**a samu kansu mafi yawa a yammacin Afrika, mutane ne da s**a kafa garuruwa daban-daban, sannan duk garin da s**a kafa suna da jagoranci na sarautarsu.

Ba su samu damar haɗa kansu wuri guda ƙarƙashin tuta ɗaya ba, hakan ya sa ake kiran kowanne da sunan garinsu da kuma sunan sarautarsu.

Yana Daga Abin da ya zo A tarihi, ƙasar Hausa na da manyan garuruwa guda bakwai inda s**a fara zama A Wannan Yanki Namu Ana Kiran su da "HAUSA BAKWAI", waɗannan garuruwa sune kamar haka:
Daura
Gobir
Kano
Katsina
Zazzau
Rano
Birom.
Fitaccen masanin tarihin Hausawa, Farfesa Abdullahi Sa'id da ɗalibinsa kuma Farfesa Mahadi Adamu, sun bayyana cewa "Asalin Hausawa sun taho ne daga yankin Arewacin jamhuriyyar Nijar, wajen Agadas a yanzu, lokacin da Hamada ta fara tsanani sai neman waje mai danshi da lema da ruwa ya sa wasun su s**a fara sauya matsuguni" s**a rika komawa waɗancan garuruwa da aka lissafa a sama da ke Najeriya.

"Waɗanda s**a fara kafa tarihi a cikin Hausawa sune Daurawa da s**a bunkasa sai s**a janyo hankalin mutane da dama daga mabanbantan wurare ciki harda Larabawa", in ji farfesa Mahadi Adamu.

To masu salon Magana kan ce zama da madaukin kanwa shi ke kawo farin kai, ko da al'adunsu s**a fara cudanya sai kuma sabbin matsaloli s**a bijiro, da s**a haɗa da yunwa da kuma yake-yake, a nan ne wasunsu s**a fara hijira suna kafa wasu garuruwan da kuma sarautunsu, duk inda s**a kafa gari sai su naɗa sarautarsu, da dama suna alakanta sarautarsu da ta Daura, amma wasu ba su alakanta ba.

Farfesa Tijjani Muhammad Naniya ya ce "a wani kaulin kuma ana ganin Hausawa sun samo asali ne daga yankin gabashin Afrika, can wajen Habasha, dalili kuwa shi ne al'adun gargajiya irin na wannan wuri sun zama kusan daya da irin na Hausawa, domin kamar yadda Hausawa ke bautawa rana kafin zuwan musulunci haka su ma suke bauta wa rana, sannan kayan da suke sanyawa ma yafe ne kamar Hausawa, kana gidajensu ma na rufin bunu ne kamar yadda na Hausawa suke.

Sannan har yau har gobe akwai irin wadannan Hausawa a Habasha."

ASALIN KALMAR HAUSA DAGA MASANA DABAN DABAN:

Masana tarihi da harshe sun kawo ra’ayoyi mabamban ta game da asalin kalmar “Hausa”. Ga wasu daga cikin ra’ayoyin:
Ra’ayin Palmer
H. R. Palmer ya bayyana cewa: "kalmar Hausa ta samo asali ne daga kalmar “Habasha” ko “Habe”, wadda ake dangantawa da wasu mutane daga Gabas. Ya yi imanin cewa canjin lafazi ne ya mayar da ita “Hausa”.
Ra’ayin Barth
Heinrich Barth ya nuna cewa: "kalmar Hausa tsohuwar suna ce ta al’ummar da s**a zauna a yankin Sudan ta Yamma tun da dadewa, kuma Larabawa sun riƙa amfani da ita wajen kiran mutanen yankin".
Ra’ayin Smith
Abdullahi Smith ya bayyana cewa: "Hausawa Ba baƙin al’umma ba ne daga waje, don haka kalmar Hausa tana da alaƙa da mutanen cikin gida da harshensu tun asali".
Ra’ayin M. G. Smith:
M. G. Smith ya danganta kalmar Hausa da tsarin zamantakewa da siyasar ƙasar Hausa, yana ganin sunan ya samo asali ne daga haɗuwar al’umma masu harshe iri ɗaya.
Ra’ayin Bargery
George Percy Bargery ya nuna cewa kalmar Hausa ta daɗe tana wakiltar harshe da al’ada kafin zuwan Turawa, kuma tana nufin mutanen da ke magana da harshen Hausa.

Atakaice Da Babu Wani Jamhurin Malamai Ko Masana Tarihi Da S**a Hadu A magana Daya Kan Asalin Kalmar Hausa ko Hausawa Bari dai Kowa Yana Gina Maganar Sa Ne akan Ra'ayin sa

Allah ne Masani

AL'ADUN HAUSAWA, KASUWAN CI, ADDINI D.S:
Kasancewar Kabilar Hausa Kabila ce Mai Dogon Tarihi Da Wayewa Da Mu'amala da Wasu Kabilun Da Dama Hakan Yasa Suna da Al'adu Nasu Tun Kafin Zuwan Musulunci Hausawa Da Turawa. Waɗannan al’adu sun shafi rayuwa gaba ɗaya kamar aure, haihuwa, sana’a, sutura da zamantakewa.
1. Addini da Bautu
Hausawa sun kasance masu bautar iskoki da gumaka. Sun yi imani da:
Tsafi
Bori
Camfi
Bautar iskoki da bishiyoyi
Suna neman kariya ko waraka ta wurin boka da matsafa.
2. Sana’o’i
Hausawa sun kasance ƙwararru wajen sana’o’i kamar:
Noma
Kiwo
Jima
Rini
Saƙa
Ƙira
Fatauci
3. Aure
Auren Hausawa yana gudana ne bisa al’ada. Ana:
Neman aure ta hannun iyaye
Baiko
Sadaki
Bukukuwan aure da waƙoƙi
4. Sutura
Maza suna sanya:
Riga
Wando
Hula
Mata kuma suna sanya:
Zani
Riga
Gyale
Kayan ado na gargajiya
5. Abinci
Abincin Hausawa ya haɗa da:
Tuwo
Fura
Kunu
Dambu
Nama da madara
6. Mulki
Hausawa suna da tsarin sarauta tun da dadewa. Akwai:
Sarki
Hakimai
Masarauta
Majalisar dattawa
7. Wasanni da Nishaɗi
Suna yin:
Kokawa
Dambe
Kalangu
Waƙoƙin baka
Tatsuniya.

ILIMIN HAUSAWA :

Hausawa suna da irin nasu ilimin tun kafin zuwan Musulunci da Turawa. Wannan ilimi ya shafi yadda suke gudanar da rayuwarsu ta yau da kullum.
1. Ilimin Sana’a
Hausawa sun kware wajen koyon sana’o’i kamar:
Noma
Kiwo
Ƙira
Saƙa
Rini
Jima
Fatauci
Iyaye ne ke koya wa ’ya’yansu waɗannan sana’o’i tun suna yara.
2. Ilimin Magunguna
Hausawa sun san magungunan gargajiya daga:
Ganyaye
Saiwoyi
Itatuwa
Ƙasa da wasu abubuwan halitta
Suna amfani da su wajen warkar da cututtuka daban-daban.
3. Ilimin Taurari da Yanayi
Hausawa sun iya gane:
Lokacin damina
Lokacin fari
Yanayin noma
Ta hanyar kallon:
Taurari
Wata
Iska
Gizagizai
4. Ilimin Zamantakewa
Suna koyar da:
Ladabi
Biyayya
Girmama na gaba
Zumunci
Riƙon amana
Ana samun wannan ilimi ta tarbiyya da tatsuniyoyi.
5. Ilimin Mulki
Hausawa sun san yadda ake gudanar da mulki da shari’ar gargajiya ta hanyar:
Sarki
Hakimai
Masu unguwa
Majalisar dattawa.
6. Ilimin Adabi
Hausawa na da ilimin:
Tatsuniya
Karin magana
Waƙoƙin baka
Hikaya
Waɗannan suna koyar da hikima da darussa ga al’umma.

Atakai ce idan kayi duba na tsanaki zakaga cewa kabilar Hausa kabila ce wacce take da tsari irin nata,take da ilimi da wayewa ta mu'amala wanda ko da turawa s**azo sun sha wahala sabida sun same su da tsari na shugabanci da na addini da kuma na zamantakewa
Don haka Tabbas Dole Ka Yabawa Kabilar Hausa wajen wannan Tsari Nata.

Alhamdulillah Wassalatu Wassalamu Ala Rasulullahi
Muhadu Afitowa Ta Gaba.

Amb. Rufai Bunyamin MakwararDarul Qadereeya Jos

08/05/2026

Shekaru 43 ne Na Jihadin Dan Fodio Shekaru 30 yana kira Bilhikimati wal mau'iza Hasana Shekaru 13 na Yaki
Via. Amb.RBM

Shehu Dan Fodiye Sai Da Ya Shekara 30 Yana Kira Ga Sarakunan Hausa Da Al'ummar Su Da Su Dawo Kan Gwadabe Na Gaskiya Abau...
08/05/2026

Shehu Dan Fodiye Sai Da Ya Shekara 30 Yana Kira Ga Sarakunan Hausa Da Al'ummar Su Da Su Dawo Kan Gwadabe Na Gaskiya Abautawa Allah Shi kadai,Banda Shirka,Banda C**a, Adaina Zalunci,Adaina Zina,Adaina Shan giya, Adawo Ayi Addini Yanda Ubangiji Ya Saukar Dashi Ga Annabi Muhammadu Amma Haka Ya shafe Shekaru 30 Sunki Amsa Kiram Sa Babu Wani nau'in Cutarwa Wacce Basuyi Masa Ba Dashi Da Sahabban Sa

Tamkar Yanda Mushrikan Maka S**a ringa Cutar Ga Shugaban Mu Alaihiisssalatu Wassalam

Lallai Shehu Usman Bn fodiye Ya Zama Magajin Manzon Allah (SAW)

بسم الله الرحمن الرحيم     وصلى الله على النبي الكريم.                       GABATARWA:       "DAULAR DAN FODIYE JIYA DA...
06/05/2026

بسم الله الرحمن الرحيم وصلى الله على النبي الكريم.

GABATARWA:

"DAULAR DAN FODIYE JIYA DA YAU"

Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai, Salati Da Taslimi Su Tabbata Ga Fiyayyen Halitta Shugaba Jagaba Annabi Muhammadu Sallallahu Alaihi Wa Sallama Da Alayen Sa Da Sahabban Sa Da Masu Biye Musu Tsarkaka Har izuwa Ranar Alkiyama.
Bayan Haka,
Hakika Muntsinci Kan mu A wani zamani Da Wasu Mutane Suke Kokarin Kunna fitina Tsakanin Kabilun Hausa Da Fulani Da kudin su, da jikin su, Suna Kokarin Lallai Sai Sun Karkatar Da Manufar Jih@din Shehu Usman Bn Fodiye Da Yayi Shi Cike Da Gaskiya Da Kuma Tsoron Allah Izuwa Wata Manufa Ta Daban Ko Ta Ta'addanci da makamancin Hakan-Wal iyazu Billah- Wanda Idan Har S**a Samu Damar Hakan To Tabbas Sun Sami Wata Gaba da Zasu Kunna wutar Rigima A Wannan Yanki Na Mu Na Kasar Hausa Wacce Babu Mai Kashe Ta Sai Allah.

Idan Muka Kalli Kalmar Jih@di shi ne yaƙi Dan Daukaka Addinin Musulunci wanda Kuma Aiki ne Mai Matuƙar Muhimmanci Da Kuma Tarin Lada A Addinin Musulunci. Tun kafin Bayyanar Shehu A Ƙasar Hausa An Samu Wasu Malamai Da S**a yi Yunƙurin Wannan jIh@di A Ƙasar Hausa Amma Dai Allah Bai Basu Ikon Kafa Daula Ba Har Sai Da Shehu Usmanu ya zo.
Malamai irin su Shehu Jibirilu Dan Umar, Mal Usmanu Binduwa d
Da Kuma Sheikh Abdulkarim Almagili, Sun yi Nasu Koƙarin, Amma Dai Allah cikin HIkimar sa ya nufi cewa, Shehu ne zai wannan Aiki.

Wannan Jih@di na Shehu Usmanu Bn Fodiye An yi shi A Cikin Shekaru 43 (1188 – 1231 hijra), Wanda Ya fara Daga Garin Ɗagel, Ya kuma Kare A g
Garin Sakkwato. Shekaru 30 Na Kira Izuwa Addinin Allah Da Hijrah, Shekaru 13 kuma na yaƙi.

Asabida Duba Da Wannan Yanayi Da Muka Tsinci Kan Mu Aciki Na Tabarbarewar Zamani Na Kudiri Aniyar Yin Wannan Rubutu Tare Da Ambaton Sa Da Suna "DAULAR DAN FODIYE JIYA DA YAU"

MANUFOFIN RUBUTU:

1-Inganta Ilimin Tarihin Daular Dan Fodiye.

2-Bayyana Bangarori Masu Matsala Alokacin Jih@din Dan Fodiye Tare Da Wayar Da Kan Al'umma Game Da Rayuwar Addini Da Siyasa Acikin Wannan Daula.

3-Warware Shubhohi Da Aka Raba su Cikin Tsarin Jih@din Dan Fodiye Wanda Ba su Da Asali Ko Tushe Acikin Wannan Tafiya.

4- Fahimtar Da Al'umma Tsarin Mulki A Daular Dan fodiye.

5- Alakar Fulani Da Hausawa A Daular Dan fodiye Tare Da Sauran Kabilu.

Muhimmancin Bahasi:

Wannan Bahasi Zai Amfanar da Matasa masu kokarin neman Ilimi da Suke da Kishirwar Fahimtar Gaskiyar Abinda Ya faru Ajih@din Dan Fodiye, Hakanan zai Taimaka Wajen Daidaito Tare Da Inganta Kyakykyawan Fahimta Tsakanin Hausawa da Fulani, Tare Da Tona Asirin Masu Kokarin Kunna wuta Tsaknin Hausa Da Fulani a wannan Yanki Namu.

Abubuwan Da S**a Janyo Hankalin Mai Binkice izuwa wannan rubutu:

1-Yunkurin wayar da kan mutane Ga Barin Goyon Bayan Mutanen da Suke kokarin sai Sun Kunna Rigimar Kabilanci tsakanin Hausa da Fulani.

2-Kara Fito Da daraja Da Girman shehu dan fodiye A Idon Duniya.

3-Karancin Littattfan Da Suke Bayani Kan Daular Dan Fodiye Da Salon Ta Wajen Daukaka Addinin Islama Cikin Harshen Hausa.

4-kwadayin Mai Binkice Na Bayyanar Da Gaskiyar Abinda y
ya Faru
Tsakanin Daular Dan fodiye da Masarutun Kasar Hausa.

Iyayakar Binkice:

Daular Dan Fodiye Da Tasirin ta A Rayuwar Al'umma Daga Kafuwar ta zuwa Yau.

Tsarin binkice :

Salon Tankade da Rairaya Da Bayani.

SADAUKANTAR WA:

Na Sadaukar Da Wannan Rubutu Nawa Izuwa Ruhin Shehu Dan Fodiye Tare Da Dukkan Wanda Ya Taimaka Masa Wajen Daukaka Addinin Allah,Hakana Izuwa Ruhin Maulana Amirul Jaishi Sheikh Nasir Kabara Tare Da Khalifhan Sa Sheikh Qaribullah Kabara, Har Wa Yau Dai Izuwa Ruhin Mahaifa na Wanda S**ayi Sanadin Zuwa Na Wannan Gida Na Duniya Sheikh Bunyamin Muhammad Usman Makwarari(RTA) Tare Da Mahaifiya ta Sayyida Khadijat Muhammad Tare da Yan uwana Musamman Dr. Nasir Bunyamin Da Abubakar Bunyamin D.s, Hakana Izuwa Yan Uwa Abokai na Musamman Wanda Muke Tare Da Su A QADIRIYYA MEDIA TEAM, Hakana Izuwa Shauran Al'ummar Musulmi Musamman Mabiya Darikar Mu Ta Qadiriyya Allah Ya sakawa Kowa Da Alkhairi.

Alhamdulillah Wassalatu Wassalamu Ala Rasulullahi

Muhadu Afitowa Ta Gaba

Amb. Rufai Bunyamin Makwarari.

06/05/2026

A Kaf Mujahid@n Da Ke Yankin Afrika Babu Wanda Yayi Jih@din Dake Cike Da Gaskiya Da Rikon Amana Irin Dan Fodio
Via: Amb.RBM

Mai Alfarma Khalifhan Mujaddidi Uban Musulmin Migeria Alh. Sa'adu Abubakar III Sultan Of SokotoSarkin Musulmin Nigeria M...
06/05/2026

Mai Alfarma Khalifhan Mujaddidi Uban Musulmin Migeria

Alh. Sa'adu Abubakar III Sultan Of Sokoto
Sarkin Musulmin Nigeria Magajin Shehi Dan Fodio

Allah yayi Ruko Da Hannun Ku

Address

Makwarari
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daular Dan Fodio Jiya Da Yau posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category